Saturday, May 30, 2026
  • Home
  • Politics
  • News
  • Business
  • Culture
  • National
  • Sports
  • Lifestyle
  • Travel
  • Opinion
PeriscopeNGA.com
  • Home
  • News
  • Politics
  • Business
  • Culture
  • Opinion
  • Lifestyle
  • Contact
No Result
View All Result
PeriscopeNGA.com
Home News

Sabuwar Dangantaka Tsakanin Turai da Afirka? Faransa Ta Nuna Sabuwar Hanya, Afirka Kuma Na Jiran Hujja

Chima by Chima
May 30, 2026
in National, News, News
0
Sabuwar Dangantaka Tsakanin Turai da Afirka? Faransa Ta Nuna Sabuwar Hanya, Afirka Kuma Na Jiran Hujja
1k
VIEWS
Share on FacebookShare on Twitter

 

Daga Ipole Amajama

Related posts

Taraba guber: Ex-Labour minister emerges PDP candidate

Taraba guber: Ex-Labour minister emerges PDP candidate

May 30, 2026
1k
Taraba: APGA Reps candidate pledges economic transformation for grassroots dev’t

Taraba: APGA Reps candidate pledges economic transformation for grassroots dev’t

May 30, 2026
1k

Tsawon shekaru masu yawa, dangantakar Afirka da ƙasashen waje ta kasance cikin wani yanayi mai maimaituwa: ana shirya taruka, shugabanni su taru, su yi musayar gaisuwa da kalaman diflomasiyya, a fitar da sanarwar da ba ta da takamaiman matakai, sannan kowa ya koma gida ba tare da wani gagarumin sakamako ba. Irin waɗannan taruka sau da yawa suna kama da wasan kwaikwayon diflomasiyya fiye da hanyoyin samar da sauyi na hakika.


Ƙasar da ta shirya taron tana ƙoƙarin nuna kanta a matsayin mafi alheri fiye da sauran abokan hulɗa, yayin da shugabannin Afirka ke halartar taron cikin sanin cewa da wuya wani abu ya sauya. Wannan yanayi ya haifar da rashin amincewa, domin muhimman buƙatun Afirka kamar masana’antu, ababen more rayuwa da samar da ayyukan yi suna ci gaba da kasancewa ba a magance su yadda ya kamata ba.
A cikin wannan yanayi ne taron Africa Forward Summit da aka gudanar a Nairobi, ƙarƙashin jagorancin Shugaban Kenya, William Ruto, da Shugaban Faransa, Emmanuel Macron, ya fito a matsayin wani sabon salo. A karon farko, wata babbar ƙasar Turai ta amince da raba jagorancin wani taro da shugaban Afirka a nahiyar Afirka kanta. Wannan ya nuna wani yunƙuri na sauya salon diflomasiyyar da ta dogara da nuna iko zuwa wanda ya fi kama da haɗin gwiwa na gaskiya.
Sanarwar saka hannun jari na dala biliyan 24 ta ƙara wa wannan alama ƙarfi, tana nuna cewa Turai, musamman Faransa, na iya fara fahimtar abin da Afirka ke bukata.
Ba kamar tarukan baya ba, an gabatar da Africa Forward a matsayin dandalin kasuwanci da nufin samar da yarjejeniyoyi kai tsaye tsakanin kamfanonin Afirka da na Turai. Wannan hanya ce mai muhimmanci. Abin da Afirka ke bukata ba ƙarin kalaman abota ba ne, illa masana’antu, hanyoyi, tashoshin samar da wutar lantarki da kuma abubuwan more rayuwa na zamani.
Abu mafi jan hankali shi ne mayar da hankali kan haɗin gwiwar saka hannun jari da kuma samar da kayayyaki tare. Wato kamfanonin Turai su yi aiki tare da na Afirka wajen gina masana’antu a cikin Afirka. Idan aka aiwatar da hakan yadda ya kamata, zai iya zama farkon wani sabon fafatawa ba don kwashe albarkatun Afirka ba, sai dai don ci gabanta.
Misali, a Najeriya, babban kamfanin otal-otal na Faransa, Accor, tare da Shoreline Group na Afirka sun rattaba hannu kan wata yarjejeniya da nufin samar da katafaren tsarin otal na ƙasa na farko a Najeriya, tare da saka hannun jari na dala miliyan 300. Wannan ba tallafi ba ne kuma ba cin moriyar albarkatu ba ne. Haɗin gwiwa ne mai anfani ga kowa. Najeriya za ta samu ayyukan yi, ci gaban ababen more rayuwa da bunƙasar yawon buɗe ido, yayin da Accor za ta samu damar shiga wata kasuwa mai girma da ke ci gaba da faɗaɗa.
Irin waɗannan yarjejeniyoyi ne ke nuna cewa abokin hulɗa na gari ba shi ne wanda aka fi so ba, sai wanda yake kawo anfani na zahiri.
Ba za a iya fahimtar rawar da Faransa ke takawa a Afirka ba tare da duba tarihinta mai cike da cece-kuce ba. Mulkin mallaka na iya zama tarihi, amma tasirinsa har yanzu yana nan. Yawancin ƙasashen Afirka masu amfani da harshen Faransanci sun dogara sosai da Paris wajen harkokin tsaro, har ta kai ga wasu lokuta suna sadaukar da wani ɓangare na ikon mallakarsu domin samun kariya.
Faransa kuma ta amfana da wannan matsayi, tana ci gaba da tasiri a kan waɗannan ƙasashe ko bayan samun ‘yanci. Wannan ya haifar da wata dangantaka mai cike da ruɗani da dogaro fiye da kima.
Mali misali ne mai kyau. A shekarar 2013, sojojin Faransa sun samu yabo a matsayin masu ceto bayan sun dakile barazanar ‘yan ta’adda da ke kokarin mamaye Bamako. Amma bayan shekaru kaɗan, gwamnatocin mulkin soja sun juya wa Faransa baya, suna kallonta a matsayin matsala maimakon mafita.
Wannan ya nuna haɗarin gina dangantaka bisa dogaro da kariyar soja maimakon haɗin gwiwar tattalin arziki. Afirka ta gaji da tsarin kariya, cin zarafin sojojin haya da kuma sabon salon mulkin mallaka ta fuskar tattalin arziki wanda ke bai wa wasu damar mallakar muhimman kadarori kamar tashoshin jiragen ruwa da filayen jiragen sama.
Abin da nahiyar ke nema yanzu shi ne abokan hulɗa, ba masu kula da ita ba.
Akwai darussa masu muhimmanci a nan gaba. Ko da yake yanayin Najeriya ya bambanta da na Mali, darussan suna da amfani ga dukkan nahiyar: ƙasashen waje ba mala’iku ba ne kuma ba shaidanu ba ne. Ya kamata a ɗauke su a matsayin abokan hulɗa kuma a auna su gwargwadon irin yarjejeniyoyin da suke kawowa.
Afirka ba ta bukatar komai face tattaunawa ta gaskiya da anfani ga kowane ɓangare.
Wannan hangen nesa mai ma’ana yana da matuƙar muhimmanci. Afirka ba za ta iya ci gaba da rayuwa cikin mafarkin alheri daga wasu ba, haka kuma ba za ta yarda da cin zarafi da ake ɓoye shi da sunan abota ba. Dole shugabanninta su shiga tattaunawa cikin basira da hangen nesa, tare da tabbatar da cewa kowace yarjejeniya tana tallafawa masana’antunta da ci gabanta.
Matakin Faransa yana da muhimmanci ba ga Afirka kaɗai ba, har ma ga Turai. Ta hanyar gabatar da kanta a matsayin ƙofar shiga kasuwar Tarayyar Turai, Faransa na ba kamfanonin Afirka damar shiga wata babbar kasuwa. A lokaci guda kuma, Turai na fuskantar matsalolin raguwar yawan jama’a da kuma ƙalubalen tattalin arziki daga Asiya da Amurka, don haka tana bukatar sabbin kasuwanni.
Afirka, tare da dimbin matasanta da damar ci gaba da ke cikinta, ita ce mafi dacewa wajen wannan haɗin gwiwa.
Idan Turai ta rungumi tsarin da ke ƙarfafa kasuwanci da haɗin gwiwar samar da kayayyaki, amfanin hakan zai zama babba. Afirka za ta samu jarin da take bukata domin rage talauci, yayin da Turai za ta samu damar bunƙasa tattalin arzikinta.
Sai dai kuma Afirka ta koyi yin taka-tsantsan. An yi alkawura da dama a baya waɗanda daga bisani suka shuɗe ba tare da an aiwatar da su ba. Kamar yadda ake cewa, kamar Saint Thomas, Afirka za ta gaskata ne idan ta gani da idonta.
Gwajin gaskiya yana cikin aiwatarwa. Shin dala biliyan 24 za su zama masana’antu, hanyoyi da cibiyoyin fasahar zamani? Shin za a ga ƙarin ayyukan haɗin gwiwa a fannoni kamar basirar wucin gadi, noma da makamashi mai sabuntawa? Ko kuwa wannan taro zai zama wani sabon shafi ne a kundin alkawuran da ba a cika ba?
Afirkawa za su ci gaba da sanya ido sosai. Za su duba ci gaba a fannonin ababen more rayuwa, masana’antun sarrafa abinci da fasaha. Za su auna nasara ba da yawan jawabai ba, sai da yawan ayyukan yi da aka samar, masana’antun da aka gina da kuma talaucin da aka rage.
Taron Africa Forward na iya zama wani babban sauyi a tarihi. Ta hanyar haɗa kai da Kenya wajen jagorancin taron, Faransa ta amince da muhimmancin Afirka da ikon ta. Ta hanyar mayar da hankali kan haɗin gwiwar saka hannun jari, ta nuna fahimtar buƙatar Afirka na bunƙasa masana’antu. Alkawarin biliyoyin daloli kuma ya nuna wani mataki na ƙwarai.
Idan aka cika waɗannan alkawura, Turai da Afirka za su iya shiga wani sabon zamani na haɗin gwiwa wanda ba zai dogara da dogaro ko nuna iko ba, sai dai da ci gaba da wadata ga kowa.
Ga Afirka, saƙon a bayyane yake: a yi tattaunawa cikin ƙarfi, a nemi anfani na zahiri, kuma a ƙi duk wani salon kariya da ke tauye ‘yanci. Ga Turai kuma, damar tana a sarari: ta rungumi Afirka a matsayin abokiyar hulɗa, ba ɗaliba ba, tare da saka hannun jari a makomarta.
Tambayar ita ce: Shin Turai, musamman Faransa, ta fahimci abin da Afirka ke bukata?
Amsar wannan tambaya ba za ta fito daga jawabai ko sanarwa ba. Za ta bayyana ne a cikin masana’antun da za a gina a faɗin Afirka, a cikin otal-otal da za su karɓi baƙi, da kuma cibiyoyin fasaha da za su horar da matasa masu kirkire-kirkire.
Har sai lokacin da alkawura suka zama gaskiya, Afirka za ta ci gaba da sa ido, tattaunawa da neman hujja. Kuma sai lokacin da ayyuka suka maye gurbin kalamai ne za a iya cewa Turai ta fahimci abin da Afirka ke tsammani.
Amajama, mai sharhi kan al’amuran jama’a, yana rubutu daga Abuja.

Amajama, mai sharhi kan al’amuran jama’a, yana rubutu daga Abuja. Imel: amajamaip@gmail.com.

Tags: Afirka Kuma Na Jiran HujjaSabuwar Dangantaka Tsakanin Turai da Afirka? Faransa Ta Nuna Sabuwar Hanya
Previous Post

Taraba guber: Ex-Labour minister emerges PDP candidate

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

BROWSE BY CATEGORIES

  • Advertorial
  • Agriculture
  • Appointment
  • Business
  • Columns
  • Covid-19
  • Crime
  • Culture
  • Development
  • Education
  • Family Planning
  • Features
  • Finding Purpose with Oluwatimileyin
  • Health
  • Interview
  • Investigation
  • Keeping It Real With Nneka
  • Lifestyle
  • Malnutrition
  • National
  • News
  • News
  • NYSC
  • Opinion
  • Opinion/Letter
  • Pillow Talks With Keziah
  • Politics
  • Responsible Parenting with Oluwatobi Akintola
  • Sport
  • Sports
  • Technology
  • Travel
  • Water, Sanitation and Hygiene

BROWSE BY TOPICS

#Gombe 000 2022 2023 2027 Abia Abuja Adamawa Again Apc Bauchi by Austen Akhagbeme by Ben Ngwakwe by Citizen Bolaji O. Akinyemi By Douglas Ogbankwa by Erasmus Ikhide by Hassan Gimba by Tony Erha Campaign CBN Commissioner Edo 2024 ekiti state FG Gombe Gombe Gov Gombe State Gov Yahaya Group Inec insecurity Kaltungo Mailantarki nigeria NNPP North-East NYSC others Pdp Police Qatar Taraba Tinubu USAID women
  • About
  • Advertise
  • Careers
  • Contact

© 2023 PeriscopeNGA.com - Periscope Nigeria | Website by Sociopact.

No Result
View All Result
  • Home
  • Politics
  • News
  • Business
  • Culture
  • National
  • Sports
  • Lifestyle
  • Travel
  • Opinion

© 2023 PeriscopeNGA.com - Periscope Nigeria | Website by Sociopact.

Loading Comments...

    Jojobet GirişJojobet GirişcasibomMadridbetbetgaranti girişMarsbahis GirişGrandPashaBet destekDeneme bonusu veren siteler 2026jojobet girişCasibom Giriş